fidelitybank

Ba za mu yarda da ƙarin farashin man fetur ba- Ƙungiyar Ƙwadago

Date:

Kungiyar Kwadago ta ƙasa, NLC, ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi watsi da shirin ƙara farashin man fetur a Nijeriya.

Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Kwamared Ayuba Wabba ne ya yi wannan kiran a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Abuja a yau Alhamis.

A cewarsa, Manajan Darakta na Kamfanin Man Fetur na Nijeriya, NNPC, Mele Kyari, ya sanar da cewa farashin man fetur zai iya yin tashin gwauron zabi har N340 daga watan Fabrairun 2022.

Amma da ya ke maida martani ta sanarwar, Wabba ya baiyana matakin da gwamnatin tarayya ta ɗauka na cewa za ta riƙa baiwa ƴan Najeriya miliyan 40 Naira 5,000 a matsayin abin da zai rage musu raɗaɗin illar karuwar farashin man fetur da cewa babu hikima a ciki.

A cewarsa, jimillar kuɗaɗen da gwamnatin ta ce za ta riƙa baiwa ƴan ƙasa ya zarce kuɗaɗen da ta ce ta na kashewa a halin yanzu kan tallafin man fetur.

Shugaban na NLC ya ce duk wani yunƙuri na kwatanta farashin man fetur a Nijeriya da sauran kasashen duniya zai zama kuskure ne, inda ya suffanta yanayin da cewa “kamar ka kwatanta tuffa da mangwaro ne.”

Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa tuni ƴan ƙasa dai su ke ta tofa albarkacin bakinsu a kan wannan batu na ƙarin man fetur ta kafafen sadarwa.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp