fidelitybank

Ba za mu yarda da ƙarin farashin man fetur ba- Ƙungiyar Ƙwadago

Date:

Kungiyar Kwadago ta ƙasa, NLC, ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi watsi da shirin ƙara farashin man fetur a Nijeriya.

Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Kwamared Ayuba Wabba ne ya yi wannan kiran a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Abuja a yau Alhamis.

A cewarsa, Manajan Darakta na Kamfanin Man Fetur na Nijeriya, NNPC, Mele Kyari, ya sanar da cewa farashin man fetur zai iya yin tashin gwauron zabi har N340 daga watan Fabrairun 2022.

Amma da ya ke maida martani ta sanarwar, Wabba ya baiyana matakin da gwamnatin tarayya ta ɗauka na cewa za ta riƙa baiwa ƴan Najeriya miliyan 40 Naira 5,000 a matsayin abin da zai rage musu raɗaɗin illar karuwar farashin man fetur da cewa babu hikima a ciki.

A cewarsa, jimillar kuɗaɗen da gwamnatin ta ce za ta riƙa baiwa ƴan ƙasa ya zarce kuɗaɗen da ta ce ta na kashewa a halin yanzu kan tallafin man fetur.

Shugaban na NLC ya ce duk wani yunƙuri na kwatanta farashin man fetur a Nijeriya da sauran kasashen duniya zai zama kuskure ne, inda ya suffanta yanayin da cewa “kamar ka kwatanta tuffa da mangwaro ne.”

Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa tuni ƴan ƙasa dai su ke ta tofa albarkacin bakinsu a kan wannan batu na ƙarin man fetur ta kafafen sadarwa.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An binne marigayi Muhammadu Buhari a gidansa na Daura

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a...

Pillars ta dauki yan wasa guda biyu

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta tabbatar da...

An cafke ‘yan Daba 28 a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta samu...

Na yafe wa Buhari duk abun da ya yi min – Buba Galadima

Buba Galadima, wanda tsohon abokin marigayi Muhammadu Buhari ne...

Shugabannin Afrika za su halarci jana’izar Buhari

Ana sa ran wasu daga cikin shugabannin ƙasashen Afirka...

Yadda ake shirye-shiryen jana’izar Buhari a Daura

A yanzu haka dai alumma na ta tururuwa domin...

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...
X whatsapp