Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar na musanta zargin Isra’ila na cewa ta ƙaddamar da hare-haren makamai masu linzami bayan fara batun tsagaita wuta a yaƙin.
Isra’ila dai ta ruwaito cewa Iran ta kai mata wasu hare-hare, duk da cewa ba a samu labarin mutuwa ba, amma an tabbatar da mutum ɗaya ya jikkata.
Isra’ila dai ta yi barazanar mayar da martani kan hare-haren, inda ta zargi Iran da karya alƙawari da yarjejeniyar tsagaita wuta.
A nata ɓangaren, Iran ta ce ba za ta daina tsagaita wuta ba, har sai Isra’ila ta tsagaita.