fidelitybank

Atiku zai yi zawarcin Shekarau a Kano

Date:

Ɗan takarar shugabancin kasa a inuwar jam’iyyar PDP ta hamayya, Atiku Abubakar na shirin kai ziyara birnin Kano a gobe Lahadi domin karbar Sanata Ibrahim Shekarau a jam’iyyarsu.

Ziyarar ta Atiku da wani makusancinsa ya tabbatarwa BBC na zuwa ne adaidai lokacin da ake dakon jin matsayar Sanata Shekarau da tun a makon da ya gabata ake jita-jitar zai fice daga NNPP.

A farkon wannan makon mai ƙarewa tsohon gwamnan Kano kuma Sanata mai wakiltar Kano ta Tsakiya, Malam Ibrahim Shekarau, ya nuna alamonin raba gari da jam’iyyar NNPP.

Sanata Shekarau a wata hira da ya yi da BBC ya zargi jagoran jam’iyyar NNPP kuma ɗan takarar shugaban kasa, Rabi’u Musa Kwankwaso da yaudararsu.

Sannan ya shaida cewa suna kan tattauna da tuntubar juna domin sanar da matsayarsu kan ci gaba da zama a NNPP ko akasin haka.

Sai dai majiya mai karfi daga bangaren Atiku ta tabbatarwa da BBC cewa a gobe Lahadi Atiku zai gana da Shekarau a Kano a shirye-shiryen tabbatar da komawarsa PDP.

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp