fidelitybank

APC ta kammala shirin ƙalubalantar NNPP a Kano

Date:

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC), ta kammala shirin kalubalantar sakamakon zaben gwamnan Kano da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris a kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Kano.

Jam’iyyar ta yanke wannan shawarar ne bayan dan takararta na gwamna, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, a ranar Laraba, ya taya zababben gwamna, Engr. Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP), jim kadan bayan ya samu takardar shedar lashe zabe daga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Amma Kakakin Jam’iyyar APC a Kano, Ahmed Aruwa, a ranar Asabar, ya yi nuni da cewa, jam’iyyar ta umurci tawagar lauyoyin ta da su fara gudanar da shari’a, inda suke kalubalantar sakamakon zaben da ya baiwa dan takarar gwamnan NNPP nasara, kamar yadda INEC ta bayyana.

Ya ce APC ta Kano na tuhumar NNPP, dan takararta na gwamna, da INEC.

Karanta Wannan: A dakata da baiwa gwamnatin Kano bashi – Abba

A cewarsa, “Jam’iyyar APC ta Kano ta yi watsi da sakamakon da INEC ta bayyana, wanda ya tabbatar da dan takarar jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna.”

Ya kara da cewa ayyana wanda ya lashe zaben kamar yadda INEC ta sanar ya sabawa dokokin da suka tsara yadda za a gudanar da zaben baki daya.

Aruwa ya bayyana cewa, shugabannin jam’iyyar na jihar sun umarci hukumar da ta ci gaba da kalubalantar sakamakon zaben a gaban kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar da ke zamanta a harabar kotun Miller.

A cewarsa, duk da cewa dan takarar gwamna na jam’iyyar APC, Gawuna, ya taya zababben gwamnan murna, “Jam’iyyar APC na da yakinin cewa wannan shelar ya saba wa dokokin zabe da aka shimfida, wanda ya sa APC ta yanke shawarar ci gaba domin neman hakkin shari’a a gaban kotu mai hurumin da ya dace”.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp