Wasu daga cikin jiga-jigan jam`iyyar APC sun ce ya kamata jam`iyyar ta mika takarar shugabancin ƙasar a zaɓen 2023 ga yankin kudancin ƙasar.
Masu irin wannan ra`ayin na cewa yin hakan shi ne adalci ga Kudancin ƙasar, tunda ɗan Arewa, wato shugaba Muhammadu Buhari ne ya samu wa`adin mulki biyu a ƙarƙashin tutar jam`iyyar, domin haka a sake tsayar da ɗantakara daga yankin Arewa zai zamanto tauye haƙƙin ƴan Kudu.
Sanata Mohammed Ali Ndume, ɗan majalisar dattawan ƙasar ne mai irin wannan ra`ayin, kuma ya shaidawa BBC cewa ya kamata ya kasance an gina jam’iyyar APC a kan adalci, irin wanda aka yi lokacin da aka nemi Arewa ta bayar da ɗan takara.
A cewarsa, ”Haka aka yi har aka goyi bayan shugaba Muhamadu Buhari, mutum ɗaya ne daga Kudu wato Rochas Okorocha ya fito daga kudu, kuma shima ya fito ne a ra’ayin kansa ba tare da goyon bayan jam’iyya ba, shi yasa ma bai samu nasara ba”.