A na tuhumar wasu ‘yan kasar Uganda da laifin kisan kai, bayan da aka kashe wani mutum a birnin Kampala bayan da rikici ya barke tsakanin magoya bayan wasu kungiyoyin kwallon kafa na gasar firimiyar Ingila.
Wani kansila ya rasa ransa a sanadiyyar raunukan da ya samu daga wukar da aka daba masa yayin da yake kokarin raba fada tsakanin wasu magoya kungiyoyin kwallon kafa, bayan da kungiyar Arsenal ta sha kaye a hannun Manchester City a wasan da suka buga ranar Juma’a.
Karanta Wannan:Â An sallami magoya bayan Arsenal da aka kama a bayan sun doke Man United
Kansilan mai suna Allan Kakumba ya mutu ne jim kadan bayan an kai shi asibiti, kamar yadda jaridar Daily Monitor ta ruwaito.
Cikin wata sanarwar da suka fiyar, ‘yan sanda sun ce tuni aka kama mutanen da ke da hannu kan kisan kansilan.