fidelitybank

Ana samun ɓullar Omicron a Nijeriya, Shugaban Ƙasar Afirka ta Kudu ya bazamo zuwa Nijeriya

Date:

 

Yayin da ƙasar Nijeriya ta shiga fargabar ɓullar hatsabibin nau’in cutar koronan nan da a ka yiwa laƙabi da Omicron, kwatsam sai ga Shugaban Ƙasar Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa ya bazamo zuwa ƙasar nan.

Bayan da Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa an samu mutane 2 ɗauke da sabon nau’in koronan a ƙasar nan, ba a daɗe ba sai a ka ƙara samun wani ɗauke da ita, duk a yau Laraba.

Da ma ita wannan Omicron ɗin dai ta samo asali ne daga Afirka ta Kudu, kuma bincike ya nuna cewa waɗan nan masu ɗauke da ita a ƙasar nan ɗin daga kasar su ka shigo Nijeriya.

Ai kuwa sai ga shuganan ƙasar ta Afirka ta Kudu, Ramaphosa ya falfalo wajen Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

Shi kuwa Buhari, Ramaphosa ya na isowa da misalin ƙarfe 10 na safe, sai ya sa a ka buga masa fareti sannan a ka harba bindigar ban-girma sau 21.

A na tunanin ya zo ƙasar nan ne domin su tattauna da shugaba Buhari a kan yadda za a haɗa karfi waje guda domin a shawo kan lamarin.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp