fidelitybank

An ƙone mana matafiya amma Buhari ya tafi Legas bikin ƙaddamar da littafin da ba Kur’ani ko Bible ba – Bafarawa

Date:

 

Tsohon gwamnan Jihar Sokoto, Attahiru Bafarawa ya baiyana ɓacin ransa a kan Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari sakamakon rashin zuwa ya jajantawa al’ummar jihar kan ƙona matafiya 42 da ƴan ta’adda su ka yi.

A wata hira da BBC Hausa ta yi da shi a jiya Asabar, Bafarawa ya ce Buhari ya gaza magance rashin tsaro da ke addabar jihohin Zamfara, Sokoto da Katsina.

Bafarawa ya baiyana cewa shugaba Buhari ba ya daraja rayukan al’ummar da su ka zaɓe shi.

“Abin da ya fi damu na shine yadda a ka maida rayukan al’umma basu da wata daraja. Ka duba rayukan da su ka salwanta a kwanaki 5 ko 6 da su ka gabata.

“An harbe mutane sannan a ka ƙone su a cikin mota amma Buhari ya tafi Legas bikin ƙaddamar da littafi, littafin da ba Kur’ani ko Bible ba.

“Bai zo Sokoto ya mana ta’aziya ba sai dai kawai ya turo wakilai.

“Lokacin da ya ke kamfen neman zaɓe ai da kansa ya zo, ba aikowa ya yi ba, sabo da ya na neman kuri’a.

“Me ya hana shi zuwa yai mana ta’aziya da jaje, amma ya tafi Legas wajen kaddamar da littafi? Mu dai kawai sai dai mu ce Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Raji’un. Sabon Birni, Shinkafi, Goronyo na cikin mawuyacin hali.

“Mu dai kawai sai dai mu ci gaba da addu’a a kan Allah Ya yaye mana Ya kuma kare mu,” in ji Bafarawa.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp