fidelitybank

An ƙone mana matafiya amma Buhari ya tafi Legas bikin ƙaddamar da littafin da ba Kur’ani ko Bible ba – Bafarawa

Date:

 

Tsohon gwamnan Jihar Sokoto, Attahiru Bafarawa ya baiyana ɓacin ransa a kan Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari sakamakon rashin zuwa ya jajantawa al’ummar jihar kan ƙona matafiya 42 da ƴan ta’adda su ka yi.

A wata hira da BBC Hausa ta yi da shi a jiya Asabar, Bafarawa ya ce Buhari ya gaza magance rashin tsaro da ke addabar jihohin Zamfara, Sokoto da Katsina.

Bafarawa ya baiyana cewa shugaba Buhari ba ya daraja rayukan al’ummar da su ka zaɓe shi.

“Abin da ya fi damu na shine yadda a ka maida rayukan al’umma basu da wata daraja. Ka duba rayukan da su ka salwanta a kwanaki 5 ko 6 da su ka gabata.

“An harbe mutane sannan a ka ƙone su a cikin mota amma Buhari ya tafi Legas bikin ƙaddamar da littafi, littafin da ba Kur’ani ko Bible ba.

“Bai zo Sokoto ya mana ta’aziya ba sai dai kawai ya turo wakilai.

“Lokacin da ya ke kamfen neman zaɓe ai da kansa ya zo, ba aikowa ya yi ba, sabo da ya na neman kuri’a.

“Me ya hana shi zuwa yai mana ta’aziya da jaje, amma ya tafi Legas wajen kaddamar da littafi? Mu dai kawai sai dai mu ce Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Raji’un. Sabon Birni, Shinkafi, Goronyo na cikin mawuyacin hali.

“Mu dai kawai sai dai mu ci gaba da addu’a a kan Allah Ya yaye mana Ya kuma kare mu,” in ji Bafarawa.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...
X whatsapp