Rahotanni na nuni da cewa a kalla wasu yara su 14 sun rasa rayukan su, sakamakon wata babbar mota da hau ta kan su.
Lamarin ya faru ne a yankin Bundun a Saminaka da ke karamar hukumar Lere a jihar Kaduna, a daren ranar Alhamis.
Yaran sun gamu da ajalinsu ne a lokacin da su ka je aikin roron wake a gona, inda babbar motar ta kwace ta kuma bi takan yaran su ka mutu har lahira. A cewar Aminiya.