Gwamnatin jihar Kano, ta bayar da umarnin tono gawar wani almajiri wanda ake zargin malaminsa ya halaka shi ta hanyar duka.
Kwamishinan Harkokin Addinai Dr. Muhammad Tahar Adamu (Baba Impossible) ne ya bayyana hakan yayin da ya jagoranci bankado makarantar ’yan marin da ke unguwar Wailari a yankin Na’ibawa.
Aminiya ta rawaito cewa, ana zargin malamin da yi wa almajirin dukan kawo wuka, lamarin da ya yi ajalinsa.
Haka kuma rahotanni sun bayyana cewa lokacin da almajirin ya rasu ba a sanar da iyayensa ba aka je aka binne shi.
Baba Impossible ya bayyana cewa, gwamnatin ta sa ’yan sanda su hako gawar almajirin tare da gudanar da bincike, domin gano musabbabin rasuwarsa.
Da yake nasa jawabin, mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa a yanzu haka mai makarantar da sauran wadanda ke taimaka masa suna hannu, domin fadada bincike a kai tare da rufe makarantar.