fidelitybank

An kuma ƙwata wa: Tankar mai ta yi bindiga yayin da ƴan ganima su ka mamaye ta

Date:

Ana fargabar mutane da yawa sun rasu wasu kuma sun ji rauni yayin da suke kokarin dibar man fetur daga wata tankar mai da ta fadi a kwanar Dikko da ke, babban titin Abuja zuwa Kaduna, a jihar Naija.

Rahotanni na cewa lamarin wanda ya faru yau Asabar, ya kasance ne lokacin da tankar da ke gudu ta fadi man ya zube, mutane suka je suna kwasar man sai motar ta yi bindiga wuta ta tashi.

Wutar ta kone mutane da dama da ke kwasar man yayin da wadanda suke nesa da ita kuwa suka ji rauni.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, Bologi Ibrahim, wanda shi ne kakakin gwamnan jihar ta Naija, Mohammed Bago, wanda ke cikin tawagar gwamnan da ke kan hanyarta ta zuwa Suleja da Tafa domin duba ayyuka, ya tabbatar mata da aukuwar lamarin.

Kakakin ya ce gwamnan ya nuna alhininsa a kan hadarin sannan ya bayar da umarni ga jami’an tsaro su tabbatar da tsaro a wajen sannan dukkanin hukumomin gwamnatin jihar su yi abin da ya wajaba a kai.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...

Bajintar ɗaliban Najeriya a gasar Turanci ta nuna ingancin ilimi a ƙasa – Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya taya ƴanmatan nan uku...

Ƙudirin faɗaɗa mamayar Gaza zai ƙara jefa Falasɗinawa cikin hatsari – MDD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana rahotannin da ke kwarmata...

APC a Kano mu na jinjinawa Tinubu – Abdullahi Abbas

Shugabannin jam’iyyar APC a jihar Kano, sun yabawa shugaba...

Kwamishinan da ake tuhuma da belin dilan kwayoyi a Kano ya yi murabus

Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi ya...

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...
X whatsapp