fidelitybank

An kuma ƙwata wa: Tankar mai ta yi bindiga yayin da ƴan ganima su ka mamaye ta

Date:

Ana fargabar mutane da yawa sun rasu wasu kuma sun ji rauni yayin da suke kokarin dibar man fetur daga wata tankar mai da ta fadi a kwanar Dikko da ke, babban titin Abuja zuwa Kaduna, a jihar Naija.

Rahotanni na cewa lamarin wanda ya faru yau Asabar, ya kasance ne lokacin da tankar da ke gudu ta fadi man ya zube, mutane suka je suna kwasar man sai motar ta yi bindiga wuta ta tashi.

Wutar ta kone mutane da dama da ke kwasar man yayin da wadanda suke nesa da ita kuwa suka ji rauni.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, Bologi Ibrahim, wanda shi ne kakakin gwamnan jihar ta Naija, Mohammed Bago, wanda ke cikin tawagar gwamnan da ke kan hanyarta ta zuwa Suleja da Tafa domin duba ayyuka, ya tabbatar mata da aukuwar lamarin.

Kakakin ya ce gwamnan ya nuna alhininsa a kan hadarin sannan ya bayar da umarni ga jami’an tsaro su tabbatar da tsaro a wajen sannan dukkanin hukumomin gwamnatin jihar su yi abin da ya wajaba a kai.

vanguard 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp