fidelitybank

An kuma ƙwata wa: Tankar mai ta yi bindiga yayin da ƴan ganima su ka mamaye ta

Date:

Ana fargabar mutane da yawa sun rasu wasu kuma sun ji rauni yayin da suke kokarin dibar man fetur daga wata tankar mai da ta fadi a kwanar Dikko da ke, babban titin Abuja zuwa Kaduna, a jihar Naija.

Rahotanni na cewa lamarin wanda ya faru yau Asabar, ya kasance ne lokacin da tankar da ke gudu ta fadi man ya zube, mutane suka je suna kwasar man sai motar ta yi bindiga wuta ta tashi.

Wutar ta kone mutane da dama da ke kwasar man yayin da wadanda suke nesa da ita kuwa suka ji rauni.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, Bologi Ibrahim, wanda shi ne kakakin gwamnan jihar ta Naija, Mohammed Bago, wanda ke cikin tawagar gwamnan da ke kan hanyarta ta zuwa Suleja da Tafa domin duba ayyuka, ya tabbatar mata da aukuwar lamarin.

Kakakin ya ce gwamnan ya nuna alhininsa a kan hadarin sannan ya bayar da umarni ga jami’an tsaro su tabbatar da tsaro a wajen sannan dukkanin hukumomin gwamnatin jihar su yi abin da ya wajaba a kai.

nigeria news today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp