Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile wani harin Boko Haram a ƙauyen Warambe na karamar hukumar Gwoza na jihar Borno, inda suka hallaka mayaƙa biyar.
Warambe ɗaya ne daga cikin ƙauyukan da ke ɗauke da mutanen da aka sake mayarwa yankin, inda ƴan ta da ƙayar baya suka sha yin yunkurin afka wa ƙauyen.
Shugaban maharban yankin, wanda ya tabbatarwa jaridar Daily Trust faruwar lamarin, ya ce mayaƙan ƙungiyar sun yi wa ƙauyen tsinke ne da misalin karfe shida na yammacin ranar Juma’a.
“Sai dai sun gamu da jami’an mu inda aka yi artabu har ta kai ga biyar daga cikin ƴan ƙungiyar suka kwanta dama. Mun ƙwato makamai da harsasai waɗanda ke yanzu haka ke karkashin ikon sojoji,” in ji shi.