fidelitybank

An karawa ma’aikata albashi kwatankwacin kudin Najeriya Naira 137,500

Date:

Kasar Turkiyya ta sanar da yi wa ma’aikatanta karin albashi da kaso 50 cikin 100 a daidai lokacin da ta ke fama da hauhawar farashin kayayyaki da kuma karyewar kudin kasarta,

Shugaban kasar, Recep Tayyip Erdogan, wanda ya sanar da hakan yayin wani taron manema labarai a ranar Alhamis.

Ya ce karin shi ne irinsa mafi girma a tarihin kasar cikin shekara 50.Kuma karin dai na nufin yanzu mafi karancin albashi a kasar zai kai kudin kasar na Lira 4,250, kwatankwacin Naira 137,500, sabanin Lira 2,826 (N91,000) da ake biya a baya.

Bugu da kari, karin albashin zai shafi kimanin ma’aikata miliyan shida a kasar.

Erdogan ya ce, “Mun himmatu wajen rage wa mutane halin rashin tabbas din da suka fada sakamakon tashin gwauron zabon da kayayyaki suka yi, da kuma ci gaba da karyewar darajar kudin kasarmu.”

Shugaban ya kuma sanar da cewa kasar za ta dauke wa ’yan kasar biyan wasu kudaden haraji daga cikin sabon albashin.

Tattalin arzikin kasar Turkiyya dai na shan fama da kalubale, ta inda sai da darajar kudin kasar ta ragu da kusan rabi, in aka kwatanta ta da Dalar Amurka tun farkon watan Janairun bana. Inji Aminiya.

Alkaluman hauhawar farashin dai ya haura kaso 21 cikin 100 wanda Babban Bankin Kasar ya yi harsashe.

Sai dai jam’iyyun adawa a kasar na harsashen ta yiwu alkaluman ma sun wuce haka.

 

benue news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp