Hukumomi a jihar Zamfara sun dawo da harkokin sadarwa a yankin al’ummar ta Zamfara.
Idan dai ba a manta ba a ranar Larabar da ta gabata ne gwamnatin jihar Zamfara ta ce ana ci gaba da aikin dawo da ayyukan sadarwa a jihar.
A wani mataki na magance ‘yan fashi a jihar Arewa maso Yamma, gwamnati ta yanke hanyoyin sadarwa a kananan hukumomi 14 a watan Satumba.
Sai dai a ranar 27 ga watan Nuwamba ne, Gwamna Bello Matawalle ya ba da umarnin dawo da hanyoyin sadarwa a Gusau, babban birnin jihar.