fidelitybank

An damke Matashin da ya kashe dillalin waya a Katsina

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Litinin, ta gurfanar da wani matashi dan shekara 17 mai suna Abdulrahman Ibrahim, bisa zargin kashe wani dillalin waya a cikin birnin Katsina.

A cewar mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan, CSP Gambo Isah, ‘yan sandan sun samu nasarar cafke wanda ake zargin ne bayan da ya jawo dilalin wayar a cikin wani gini da bai kammala ba a unguwar Modoji, Katsina, ya kuma daba masa wuka a wuyansa, inda daga karshe ya mutu.

Abdulrahman Ibrahim a wata hira da manema labarai yayi zargin cewa ya kashe mutumin ne domin kare kansa.

A cewarsa, “Na kashe shi ne a lokacin da yake so ya kashe ni kuma ya raunata ni a hannu.”

A wani labarin kuma, CSP Gambo ya ce jami’an ‘yan sanda na rundunar sun kai samame a wasu maboyar ‘yan ta’adda a cikin babban birnin jihar, inda suka kama wasu mutane 72 da ake zargin barayin jama’a ne, wanda aka fi sani da Kauraye a kasar Hausa da wata dabara ta satar waya.

A cewar CSP Gambo, yankunan da aka kai samame sun hada da: Sabuwar Unguwa, Gadar Nayalli, Modoji, Tudun YanLihida, Kwabren Dorawa, Janbango, Abbatuwa, Filin Canada, Lambun Dankwai, Kofar Marusa, Tsalawa, da Chake da dai sauransu.

Rundunar ‘yan sandan ta bayyana jin dadin ta ga jama’a kan yadda suke ba ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro ‘yan uwa mata a jihar baki daya, inda ta bukace su da su rika kai rahoton duk wani mutum ko wata kungiya da suka samu matsala ga ‘yan sanda ta wadannan layukan gaggawa kamar haka: 08156977777, 09053872247.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp