‘Yan sandan sun kama mutum bakwai kan zargin cin zarafin wata mace mai shekara 40 a Jihar Enugu ta hanyar yi mata tsirara da kuma dukanta.
Cikin ƙorafin da ya aika wa ‘yan sandan, wani mai fafutikar kare haƙƙi ya ce rukunin mutanen sun afka gidan matar bayan sun zarge ta da shiga wani “daji mai tsarki” don yin farautar dodon-koɗi.
An ce mutum aƙalla 10 ne suka shiga gidan nata, inda take zaune da ‘ya’yanta huɗu da kuma mahaifiyarta.
Sun yi wa matar tsirara kuma suka tilasta mata zagaye garin suna dukanta da sanduna.
An ceto matar daga baya kuma aka kai ta asibiti, amma rahotanni sun ce tana jin jiki sosai.
Matar da maharan mazauna yankin Agunese Affam-Mmaku ne na jihar ta Enugu.