fidelitybank

An cafke mutane 17 a Zamfara

Date:

Yan sanda sun ce, sun kama mutum 17 bisa zargin laifuka daban-daban ciki har da tashe-tashen hankula bayan zaɓe, da fashin daji da satar shanu da kuma sara suka a jihar Zamfara.

A wata sanarwa da ‘yan sandan suka fitar ta hannun jami’in hulɗa da jama’a na rundunar jihar, SP Mohammed Shehu, ya ce jami’ansu sun yi kamen ne a sassa daban-daban na Zamfara, tare da ƙwato muhimman kayayyaki daga hannun waɗanda ake zargi.

Karanta Wannan: Buhari ya jinjina wa Ɗan Dambe Joshua

Rundunar ta ce daga cikin mutanen da ta kama har da wani fitaccen ɗan fashin daji wanda ya addabi jihar mai suna Sulaiman Balarabe, ɗan shekara 25.

Ta kuma ce ta kama ɗan fashin dajin – wanda da ma sunansa ke cikin jerin mutanen da rundunar ke nema ruwa-a-jallo – ranar Laraba 29 ga watan Maris

Bayan kama wanda ake zargin ne kuma, ya tabbatar wa ‘yan sanda cewa yana da hannu a hare-hare da sace mutane don neman kuɗin fansa.

Haka zalika a cewar sanarwar ‘yan sanda, Sulaiman Balarabe ya ce ya karɓi miliyoyin kuɗaɗee daga hannun imakusantan da ya sace wa ‘yan’uwansu.

Rundunar ‘yan sandan ta kuma ce ta kama ƙarin mutum uku bisa zargin satar shanu da sauran ƙananan dabbobi, a lokacin da suke kan hanyar zuwa Gusau daga Dansadau, da dabbobin a cikin motoci guda biyu.

Sanarwar ta ambato kwamishinan ‘yan sandan Zamfara, CP Kolo Yusuf na yaba wa al’ummar jihar bisa haɗin kai da suke bai wa jami’an tsaro wajen gudanar da ayyukansu.

Kwamishinan ya sake jaddada kiransa ga Zamfarawa su ci gaba da bai wa jami’an tsaron goyon baya don tabbatar da ganin kwanciyar hankali da zaman lafiya sun dawwama a jihar.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp