Bayan kwashe kwanaki 13 a hannun masu garkuwa da mutane, mahaifiyar dan majalisar dokokin Kano, Hajiya Zainab, ta shaki iskar ‘yanci a ranar Talatar, bayan an biya kudin fansa Naira miliyan 40.
Hajiya Zainab, mahaifiyar Isiyaku Ali Danja, shugaban marasa rinjaye a majalisar dokokin jihar Kano, an ce an sace ta ne daga cikin dakin kwananta da ke karamar hukumar Gezawa a jihar Kano, a ranar 12 ga watan Janairu, 2021.
Dan majalisar wanda shi ne Kakakin Majalisar Kano, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Talata, ya bayyana cewa, mahaifiyarsa ta samu ‘yanci bayan an biya shi Naira miliyan 40.
Ali Danja ya ce, ya na kan hanyarsa ta dauko mahaifiyarsa daga wata karamar hukuma a jihar Jigawa, inda masu garkuwa da mutane suka ajiye ta a wajen tun a lokacin.