fidelitybank

An ƙone mana matafiya amma Buhari ya tafi Legas bikin ƙaddamar da littafin da ba Kur’ani ko Bible ba – Bafarawa

Date:

 

Tsohon gwamnan Jihar Sokoto, Attahiru Bafarawa ya baiyana ɓacin ransa a kan Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari sakamakon rashin zuwa ya jajantawa al’ummar jihar kan ƙona matafiya 42 da ƴan ta’adda su ka yi.

A wata hira da BBC Hausa ta yi da shi a jiya Asabar, Bafarawa ya ce Buhari ya gaza magance rashin tsaro da ke addabar jihohin Zamfara, Sokoto da Katsina.

Bafarawa ya baiyana cewa shugaba Buhari ba ya daraja rayukan al’ummar da su ka zaɓe shi.

“Abin da ya fi damu na shine yadda a ka maida rayukan al’umma basu da wata daraja. Ka duba rayukan da su ka salwanta a kwanaki 5 ko 6 da su ka gabata.

“An harbe mutane sannan a ka ƙone su a cikin mota amma Buhari ya tafi Legas bikin ƙaddamar da littafi, littafin da ba Kur’ani ko Bible ba.

“Bai zo Sokoto ya mana ta’aziya ba sai dai kawai ya turo wakilai.

“Lokacin da ya ke kamfen neman zaɓe ai da kansa ya zo, ba aikowa ya yi ba, sabo da ya na neman kuri’a.

“Me ya hana shi zuwa yai mana ta’aziya da jaje, amma ya tafi Legas wajen kaddamar da littafi? Mu dai kawai sai dai mu ce Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Raji’un. Sabon Birni, Shinkafi, Goronyo na cikin mawuyacin hali.

“Mu dai kawai sai dai mu ci gaba da addu’a a kan Allah Ya yaye mana Ya kuma kare mu,” in ji Bafarawa.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp