fidelitybank

An ƙone mana matafiya amma Buhari ya tafi Legas bikin ƙaddamar da littafin da ba Kur’ani ko Bible ba – Bafarawa

Date:

 

Tsohon gwamnan Jihar Sokoto, Attahiru Bafarawa ya baiyana ɓacin ransa a kan Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari sakamakon rashin zuwa ya jajantawa al’ummar jihar kan ƙona matafiya 42 da ƴan ta’adda su ka yi.

A wata hira da BBC Hausa ta yi da shi a jiya Asabar, Bafarawa ya ce Buhari ya gaza magance rashin tsaro da ke addabar jihohin Zamfara, Sokoto da Katsina.

Bafarawa ya baiyana cewa shugaba Buhari ba ya daraja rayukan al’ummar da su ka zaɓe shi.

“Abin da ya fi damu na shine yadda a ka maida rayukan al’umma basu da wata daraja. Ka duba rayukan da su ka salwanta a kwanaki 5 ko 6 da su ka gabata.

“An harbe mutane sannan a ka ƙone su a cikin mota amma Buhari ya tafi Legas bikin ƙaddamar da littafi, littafin da ba Kur’ani ko Bible ba.

“Bai zo Sokoto ya mana ta’aziya ba sai dai kawai ya turo wakilai.

“Lokacin da ya ke kamfen neman zaɓe ai da kansa ya zo, ba aikowa ya yi ba, sabo da ya na neman kuri’a.

“Me ya hana shi zuwa yai mana ta’aziya da jaje, amma ya tafi Legas wajen kaddamar da littafi? Mu dai kawai sai dai mu ce Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Raji’un. Sabon Birni, Shinkafi, Goronyo na cikin mawuyacin hali.

“Mu dai kawai sai dai mu ci gaba da addu’a a kan Allah Ya yaye mana Ya kuma kare mu,” in ji Bafarawa.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

INEC za ta fitar da sabbin ƙa’idojin duba sakamakon zaɓe

A shirye-shiryen da take yi gabanin babban zaɓen Najeriya...

Isra’ila ta amince da sharuɗɗan yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Isra'ila ta amince...

Buhari ba zai taɓa cin amanar Tinubu ba – Garba Shehu

Tsohon babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai...

Mutane 207 ne suka mutu a ambaliyar Neja – NSEMA

Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta...

Jiga-jigan jam’iyyar PDP za su sauya sheƙa don tunkarar APC a 2027

Wasu jiga-jigan jam'iyyar PDP da suka hada da tsohon...

Za a ƙaddamar da jam’iyyar hammaya da za ta tunkari APC

Gamayyar jam'iyyun adawa a ranar Talata, ta amince da...

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...
X whatsapp