fidelitybank

Amurka ta kuduri niyar inganta shirye-shiryen kafafen yada labarai a Najeriya

Date:

Gwamnatin kasar Amurka ta ce kudurin ta na aniyar tallafawa shirye-shiryen da ke inganta da ilimin kafafen yada labarai.

Da ya ke jawabi a wajen bikin bude taron bitar a jihar Legas a ranar Litinin, jami’in hulda da jama’a na ofishin jakadancin Amurka, Stephen Ibelli ya bayyana cewa, ingantacciyar dimokuradiyya na bukatar dukkanin jama’a da a ka sa ni da kuma kafafen yada labarai masu kishin kasa wadanda ke ba da bayanai na gaskiya da gaskiya.

Shirin dai tare da goyon bayan Babban Ofishin Jakadancin Amurka a Legas da  Cibiyar yada labarai ta Afirka ta Yamma (WABMA) da Enugu Literacy Society (ELS), sun kaddamar da shirn na “Project Fact Check Nigeria,” wani aikin jarida da kuma magance rashin fahimta na zakulo bayanan gaskiya.

Aikin ya na neman ƙarfafa dabarun tunani, faɗaɗa ilimin zamani na dijital da kafofin yada labarai da haɓaka ƙarfin ƴan jaridun rediyo, domin magance munanan labarai da na ɓarna a jahohi 17 na kudancin Najeriya.

Sama da masu yada shirye-shiryen rediyo 170, ciki harda furodusoshi, da masu ba da rahoto za su sami ƙwarewar bincikar gaskiya da na mafi kyawun ayyuka, domin kaucewa yada labaran kanzon Kurege da kuma rashin fahimta.

“Ta hanyar inganta ilimin kafofin yada labarai, mu na ƙarfafa ka’idodin gaskiya, shugabanci nagari da kuma bin doka da ke aiki a matsayin ginshiƙan tsarin dimokuradiyyar mu,” inji Ibelli.

 

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp