Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya tafi kasar Amurka, domin halartar wani kwas kan harkokin sha’anin mulki.
Wata sanarwa da kwamashinan yaɗa labarai, Muhammad Garba ya fitar ranar Talata, ta ce, kwas ɗin na mako ɗaya ne mai taken Authentic Leadership Development Programme wanda Sashen Kasuwanci na Jami’ar Harvard ya shirya.
Sanarwar ta ce, gwamnan ya miƙa mulki ga mataimakinsa, Nasiru Yusuf Gawuna, wanda zai yi aiki a matsayin muƙaddashin gwamna.