Ma’aikatar lafiyar China ta bayyana cewa za ta kare “muradun ƙasarta” bayan Shugaban Ƙasar Amurka Donald Trump ya bayyana wa manema labarai cewa yana tunanin sanya harajin kashi 10 a kan dukkan kayayyakin China.
“Mun yi amannar cewa babu ƙasar da za ta ci riba idan ana jayayya da rikici kan kasuwanci ko musayar ƙaƙaba haraji,” in ji kakakin ma’aikatar, Mao Ning.
Ta ƙara da cewa “China za ta yi duk mai yiwuwa domin kare muradunta,” in ji ta.
Trump ya ce zai yiwu harajin da zai ƙaƙaba ɗin ya fara aiki daga 1 ga Fabrairu, kuma saboda China tana tura fentanyl zuwa ƙasar Mexico da Canada ne, duk da cewa China ta sha musanta zargin a baya safarar miyagun ƙwayoyi a baya.
Trump ya kuma ce zai ƙaƙaba harajin shigo da kayayyaki daga Canada da Mexico. In ji BBC.