Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya, ta yi kira ga Ministan Makamashi, Adebayo Adelabu da ya sauka saboda yawaitar katsewar babban layin lantarki na ƙasa.
A wata sanarwa da shugaban ƙungiyar, Joe Ajaero ya fitar, ya ce ƙungiyar na takaicin yadda ɓangaren lantarkin Najeriya ya ƙi gyaruwa, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Ajaero ya ce, “idan har akwai ma’aikata ƙwararru waɗanda suka san makamai aiki a ma’aikatar makamashi, to lallai za a iya kiyaye yawaitar abin kunyar nan da ake fuskanta na yawaitar katsewar layin lantarki a Najeriya. Magance matsalar ya kamata ministan ya yi, ba tiƙa maganar cewa za su magance ta ba.
“Mun yi amannar cewa wannan na nuna rashin ƙwarewa da gazawar ma’aikatar makamashin, wanda hakan ya sa muke mamakin me ya sa wanda ke jagorantar ma’aikatar ba zai sauka cikin mutunci ba.”
Ajaero ya kuma caccaki ministan bisa kasafta kashe naira biliyan 8 a kasafin kuɗin 2025 domin “wayar da kan ƴan Najeriya muhimmancin biyan kuɗin lantarki.”