fidelitybank

Al’ummar Oyo na gudanar da zanga-zanga kan tsadar rayuwa

Date:

Dubban mutane sun hau kan titunan birnin Ibdan na jihar Oyo, domin nuna fushin su kan tsadar rayuwa a Najeriya.

Zanga-zangar ta fara ne daga yankin Mokola ta birnin, inda masu yin tattakin suka yi mahaÉ—a.

Hakan na zuwa ne bayan gudanar da irin wannan zanga-zanga a jihohin Kano da Neja, inda mutane da dama suka fito domin kokawa kan matsalar tashin farashin kayan masarufi.

Al’umma a Najeriya na fama da matsalar tashin kayan masarufi ne tun bayan da shugaban Æ™asar, Bola Tinubu ya ayyana cire tallafin man fetur a ranar 29 ga watan Mayun 2023, jim kaÉ—an bayan ratsar da shi a matsayin shugaban Æ™asa.

Tun daga wancan lokacin ne farashin wasu kayan masarufi da abinci da sufuri suka nunka, lamarin da ya Æ™ara jefa al’ummar Æ™asar cikin mawuyacin hali.

Tun farko rundunar Æ´ansandan Najeriya a jihar Oyo ta gargaÉ—i masu zanga-zangar da su kauce wa duk wani abu da zai tayar da hankalin al’umma kuma ta bayyana cewa za ta tsaurara tsaro domin ganin lamarin bai rikiÉ—e zuwa tarzoma ba.

Gwamnatin Najeriya dai ta bayyana cewa tana yin duk abin da ya kamata wajen sauÆ™aÆ™a wa al’umma halin matsin na rayuwa, inda ta ayyana wani shiri na tallafin kayan abinci da na masarufi ga al’umma.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp