fidelitybank

Aisha Buhari ta baiwa Kashim Shettima muƙami a Kwalejin Future Assured

Date:

 

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Aisha Buhari, ta naɗa Kashim Shettima, tsohon gwamnan Jihar Borno, a matsayin shugaban kwamitin amintattu na Kwalejin Future Assured da ke Maiduguri.

Gidauniyar Aisha Buhari Foundation ce ta gina kwalejin a Maiduguri domin daukar nauyin karatun wadanda rikicin Boko Haram ya shafa a jihar.

Yayin kaddamar da kwamitin gudanarwa na kwalejin mai mambobi 11 karkashin jagorancin Shettima a fadar shugaban kasa da ke Abuja a ranar Talata, Aisha Buhari ta hori mambobin da su dage wajen sauke nauyin tare da sadaukarwa wajen gudanar da makarantar.

Ta ce “Na zabe ku a tsanake a matsayin mambobin kwamitin da za ku kula da harkokin gudanarwar kwalejin. Aikin na da girma, amma na yi imani za ku iya daukar nauyin.

“Saboda haka, ina addu’a cewa dukkanmu mu hada kai don cimma burinmu na saka jari a ‘ya’yanmu, mu tabbatar da makomarsu da kuma bunkasa al’umma ta hanyar yi wa bil’adama hidima.”

Ta baiyana godiya ga gwamnati da al’ummar Borno bisa goyon baya da hadin kai.

Aisha Buhari ta kuma godewa gidauniyar TY Danjuma da sauran ƙungiyoyi da suka bayar domin samun nasarar aikin.

A jawabinsa na karbar muƙamin, Shettima ya baiyana godiyarsa ga uwargidan shugaban kasar da ta ga cancantarsa ga muƙamin.

Ya bayyana kudurinsa na ganin an aiwatar da aikin ta hanyar tabbatar da cewa an kiyaye ka’idojin makarantar domin amfanin marayu.

Sauran wadanda aka nada a kwamitin sun hada da Halima Buhari-Sherrif a matsayin Sakatariya, Dr Muhammad Idris, Hadi Uba, Muhammad Albishir, Farfesa Bulama Kagu, Farfesa Aisha Ahmed, Asabe Vilita-Bashir, Dr Hajo Sani, Nana Liberty da Hauwa Ngoma.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp