fidelitybank

Aisha Buhari ta baiwa Kashim Shettima muƙami a Kwalejin Future Assured

Date:

 

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Aisha Buhari, ta naɗa Kashim Shettima, tsohon gwamnan Jihar Borno, a matsayin shugaban kwamitin amintattu na Kwalejin Future Assured da ke Maiduguri.

Gidauniyar Aisha Buhari Foundation ce ta gina kwalejin a Maiduguri domin daukar nauyin karatun wadanda rikicin Boko Haram ya shafa a jihar.

Yayin kaddamar da kwamitin gudanarwa na kwalejin mai mambobi 11 karkashin jagorancin Shettima a fadar shugaban kasa da ke Abuja a ranar Talata, Aisha Buhari ta hori mambobin da su dage wajen sauke nauyin tare da sadaukarwa wajen gudanar da makarantar.

Ta ce “Na zabe ku a tsanake a matsayin mambobin kwamitin da za ku kula da harkokin gudanarwar kwalejin. Aikin na da girma, amma na yi imani za ku iya daukar nauyin.

“Saboda haka, ina addu’a cewa dukkanmu mu hada kai don cimma burinmu na saka jari a ‘ya’yanmu, mu tabbatar da makomarsu da kuma bunkasa al’umma ta hanyar yi wa bil’adama hidima.”

Ta baiyana godiya ga gwamnati da al’ummar Borno bisa goyon baya da hadin kai.

Aisha Buhari ta kuma godewa gidauniyar TY Danjuma da sauran ƙungiyoyi da suka bayar domin samun nasarar aikin.

A jawabinsa na karbar muƙamin, Shettima ya baiyana godiyarsa ga uwargidan shugaban kasar da ta ga cancantarsa ga muƙamin.

Ya bayyana kudurinsa na ganin an aiwatar da aikin ta hanyar tabbatar da cewa an kiyaye ka’idojin makarantar domin amfanin marayu.

Sauran wadanda aka nada a kwamitin sun hada da Halima Buhari-Sherrif a matsayin Sakatariya, Dr Muhammad Idris, Hadi Uba, Muhammad Albishir, Farfesa Bulama Kagu, Farfesa Aisha Ahmed, Asabe Vilita-Bashir, Dr Hajo Sani, Nana Liberty da Hauwa Ngoma.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...

Da Ɗumi-Ɗumi: Kashim Shettima zai rako gawar Muhammadu Buhari zuwa Najeriya

Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya rasu. Ya rasu ne...

Ina Tinubu ya ke ya ɓata ba bayani – ADC

Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC, ta soki Shugaba,...

Koriya ta Arewa za ta ba Rasha ƙarin sojoji domin yaƙin Ukraine

Shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya yi...

Jam’iyyar ADC alheri ce ga siyasar Najeriya – Femi Gbajabiamila

Shugaban ma'aikata na fadar gwamnatin Najeriya, Femi Gbajabiamila ya...

Tinubu na yunkurin tauye hakkin ma’aikata – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a Najeriya, Atiku Abubakar, ya...

Trump ya lafta wa ƙasashen Tarayyar Turai da Mexico harajin kashi 30

Shugaban Amurka Donald Trump ya lafta wa ƙasashen ƙungiyar...

INEC ta ce za ta buɗe shafin intanet domin rajistar sababbin jam’iyyu

Huhukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC, ta ce nan...

EFCC na neman Rabi’u Auwalu Tijjani ruwa a jallo a Kano

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin...

An gano musabbabin hatsarin jirgin saman Indiya

Masu bincike sun bayyana sakamako na farko-farko game da...

Amurka ta haramta wa shugaban kasar Cuba shiga kasar

Amurka a karon farko ta ƙaƙaba takunkumi kan shugaban...

An kashe mutum 6,800 tare da sace 5,402 a 2025 Najeriya – Rahoto

Alƙaluma na nuna cewa an kashe mutum dubu shida...
X whatsapp