Ƙungiyar Jama’atut Tajdidil Islam, JTI, Reshen Jihar Kano, ta ce aikin Hukumar Hana Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya, NDLEA, ya yi daidai da tsarin addinin Musulunci.
Jami’in Huɗɗa da Jama’a na JTI ta Kano, Muhammad Albakary ne ya bayyana haka ne ranar Litinin a jihar Jigawa lokacin da suka kai wata ziyarar aiki ga hukumar NDLEA reshen jihar.
Al-Bakariy ya ce aikin NDLEA ya dace tsarin addinin Musulunci na hani da mu’amala da dukkan kayen maye domin kiyaye hankali da mutunci da addini.
Da ya ke mayar da jawabi, Shugaban NDLEA ta Jigawa, Ibrahim Buraje ya ce asalin kundin hukumar da aka rubuta kacokan ya bayyana tsarin addini ne na tabbatar da cewa saya da sayarwa da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi haramun ne a tsarin wannan hukuma.
Ya kuma bayyana ƙudirin hukumar na aiki hannu da hannu da JTI.
Jami’an da suka zamu zuwa ziyarar aikin sun haɗa da Isma’il Kudai wanda shi ne Shugaban Kungiyar JTI na Jihar Jigawa, Nuru Adam Galadanci, Ibrahim Rabi’u Fagge, Muhammad Zangina Kura, Umar Isma’il Ajingi, Umar Shehu Tsakuwa, Sharif Muhammad Hamza da Aliyu Ibrahim Sani Mainagge.