Mai masaukin baki Kamaru tai zazzagawa kasar Habasha kwallaye 4 da 1 raga, bayan samun nasara a gasar cin kofin nahiyar Afrika na 2021.
Wannan ya bai wa Kamaru damar shiga matakin zagaye na biyu a gasar.
Kafin karawar Kamaru da Habasha, sai da Kamaru ta kara da Burkina Faso a wasan buɗe gasar inda ta ci 2-1.
A na sa ran a ranar Litinin 17 ga watan Janairu, Kamaru za ta kara da Cape Verde a filin wasa na Olembe.