Hamshaƙin ɗan kasuwar nan a jihar Kano, Alhaji Aminu Alhassan Dantata, ya bayyana damuwar sa dangane taɓarɓarewar tsaro da ya dabaibaye Najeriya.
Alhaji Aminu Alhasaan Ɗantata ya bayyana ne hakan ne a bikin ƙaddamar da littafin “Tabswiratul Hukkam” a ɗakin taro na jami’ar Bayero a jiya Asabar.
“Hare-haren ƴan fashin daji da satar mutane domin karbar ƙudin fansa na daga cikin manyan matsalolin da yankin Arewacin Najeriya ke fama da shi”.
Ya kuma ce“Halin da ake ciki yanzu ƴan Najeriya ba su da kwanciyar hankali a kan dukiya da rayuwarsu a lokacin da su ke tafiye-tafiye ko kuma ma a gidajen su”. A cewar Ɗantata.
Alhaji Aminu shi ne ya ɗauki nauyin fassara da buga littafin na Tabswiratul Hukkam, wanda ya ke jawabi a kan shari’ar Muslunci, kuma wannan littafi zai taimakawa alkalai gudanar da jagora a lokacin gudanar da shari’o’i a kotuna.

Taron kaddamar da littafin, ya samu halarcin gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje da Mai Alfarma Sarkin Musulmi Sa’ad Abubakar III da sauran manyan baƙi daga ciki da wajen jihar Kano.