fidelitybank

Abdullahi Abbas ya zama sabon shugaban majalisar gamayyar jam’iyun siyasa

Date:

Majalisar gamayyar jam’iyun siyasa ta kasa ta zabi, shugaban jam’iyar APC, Abdullahi Abbas a matsayin shugaban majalisar reshen jihar Kano.

Da ya ke rantsar da sabbin shugabannin wakilin majalisar na kasa wanda ya jagoranci gabatar da zaben, Nasir Sidi Ali, ya ce, dukkan shugabannin an zabe su ne bayan cika dukkan ka’idojin majalisar.

Ya ce,”Dan takarar jam’iyar APC Abdullahi Abbas shi ne ya yi nasara da kuri’u 13 daga cikin kuri’u 14 da a ka kada a zaben”. In ji Nasir Sidi

A tattaunawar sa da manema labari bayan an rantsar da shi, Abdullahi Abbas ya ce, gamayyar jam’iyun karkashin jagorancinsa zai yi duk mai yuwa, domin ci gaban dimokuradaiyya.

Ya kuma ce,”Duk da cewa kowannen su ya na da jam’iyar sa, amma hakan ba zai hana mu ci gaba da aiki tare da sub a, domin ci gaban majalisar da ma jihar Kano baki da ya”. A cewar Abdullahi Abbas.

An dai zabi Abdullahi abbas na jam’iyar APC a matsayin shugaba yayin da Isa Nuhu Isa ya kasance a matsayin matemakin shugaba sai Nuhu Idris Adam na jam’iyar APM a matsayin sakatare da Abdullahi A Sharif na jam’iyar AAC a matsayin matemakin sakatare.

Sauran shugabannin sun hada da: Ado Muhammad na jami’iyar NRM a matsayin ma’aji da Bello Ado Usaini a matsayin sakataren shirye-shirye, sai sakataren kudi wanda a ka zabi Nasiru Aliko na jami’iyar ADP da Ibrahim Muhammad na jami’iyar APP a matsayin sakataren yada labarai na majalisar da kuma Salisu Umar na jami’iyar YPP a matsayin mai bada shawara a harkokin shari’a.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp