fidelitybank

Abdullahi Abbas ya zama sabon shugaban majalisar gamayyar jam’iyun siyasa

Date:

Majalisar gamayyar jam’iyun siyasa ta kasa ta zabi, shugaban jam’iyar APC, Abdullahi Abbas a matsayin shugaban majalisar reshen jihar Kano.

Da ya ke rantsar da sabbin shugabannin wakilin majalisar na kasa wanda ya jagoranci gabatar da zaben, Nasir Sidi Ali, ya ce, dukkan shugabannin an zabe su ne bayan cika dukkan ka’idojin majalisar.

Ya ce,”Dan takarar jam’iyar APC Abdullahi Abbas shi ne ya yi nasara da kuri’u 13 daga cikin kuri’u 14 da a ka kada a zaben”. In ji Nasir Sidi

A tattaunawar sa da manema labari bayan an rantsar da shi, Abdullahi Abbas ya ce, gamayyar jam’iyun karkashin jagorancinsa zai yi duk mai yuwa, domin ci gaban dimokuradaiyya.

Ya kuma ce,”Duk da cewa kowannen su ya na da jam’iyar sa, amma hakan ba zai hana mu ci gaba da aiki tare da sub a, domin ci gaban majalisar da ma jihar Kano baki da ya”. A cewar Abdullahi Abbas.

An dai zabi Abdullahi abbas na jam’iyar APC a matsayin shugaba yayin da Isa Nuhu Isa ya kasance a matsayin matemakin shugaba sai Nuhu Idris Adam na jam’iyar APM a matsayin sakatare da Abdullahi A Sharif na jam’iyar AAC a matsayin matemakin sakatare.

Sauran shugabannin sun hada da: Ado Muhammad na jami’iyar NRM a matsayin ma’aji da Bello Ado Usaini a matsayin sakataren shirye-shirye, sai sakataren kudi wanda a ka zabi Nasiru Aliko na jami’iyar ADP da Ibrahim Muhammad na jami’iyar APP a matsayin sakataren yada labarai na majalisar da kuma Salisu Umar na jami’iyar YPP a matsayin mai bada shawara a harkokin shari’a.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...
X whatsapp