fidelitybank

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Date:

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da a samar da sabon tsarin zaɓen shugaban hukumar zabe ta ƙasa (INEC), inda ya ba da shawarar kafa wani tsarin tantancewa da zaɓe mai zaman kansa don ƙara wa hukumar sahihanci kafin zaɓen gaba na 2027.

Jonathan ya bayyana wannan ra’ayi ne a ranar Laraba a Abuja, a yayin gabatar da shirin ƙasa na gyaran harkokin zaɓe, wanda Makarantar Nazarin Zamantakewa da Siyasa ta Abuja ta shirya.

Kiran ya zo ne a wani lokaci na siyasa mai ɗaukar hankali, yayin da wa’adin shugaban INEC na yanzu, Prof. Mahmood Yakubu, ke ƙarewa a watan Oktoba na wannan shekara.

Yakubu, wanda ya jagoranci zaɓukan 2019 da 2023, ya riga ya yi wa’adin aiki biyu, kuma zaɓen wanda zai gaje shi na janyo ƙarin hasashe a al’umma.

Masana na ganin cewa wanda zai zama sabon shugaban INEC zai taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da sahihancin zaɓen 2027.

Jonathan, wanda a baya an yi hasashen cewa zai iya komawa takarar shugaban ƙasa a 2027, ya ce; “Ina ganin Najeriya na iya inganta tsarin zaɓe ta hanyar kafa wani kwamitin tantancewa da zaɓe mai zaman kansa, wanda zai ƙunshi wakilai daga kotuna da ƙungiyoyin fararen hula jami’o’i da ƙungiyoyin da kwararru.”

“Wannan kwamitin zai tantance kuma ya bayar da jerin sunayen ‘yan takarar da ke neman shugabancin INEC da suka cancanta, daga cikinsu shugaban ƙasa zai iya zaɓa shugaban INEC ɗin.”

“Wannan zai rage tunanin son zuciya da ƙara amincewar jama’a da inganta sahihancin hukumar zaɓe INEC.” tsohon shugaban ƙasar ya ƙara da cewa

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp