Babbar kotun shariar Musulinci da ke jihar Kano ta bayar da umarnin tsare wasu matasa su 8 a gidan gyaran hali na jihar, sakamakon kamasu da laifin hada baki da wani karamin yaro daya sato kudin mahaifinsa Naira 3050,000 TA ATM.
A na dai zargin matasan ne da laifin hada baki da dan gidan, wanda mai kara Kawu ya shigar cewa an cire kudin mahaifinsa mai suna Abdurrahman Bawa ta hanyar hada baki da Almajirin gidan
Wadanda a ke zargin akwai wani malami mai suna, Sabo Isyaku a Na’ibawa wanda a ka bashi Naira 40,000 domin ya yi addu’a ya rufe bakin su.
Sauran sun hadar da Abubakar mai POS wanda a ka ciri 500,000 a wajensa sai Sulaiman mai POS da a ka ciri 50,000 a wajensa da kuma Muhd Sani da a ka cire Naira 100,000 a wajen sa.
A zaman kotun mai shari’a Sarki Yola, ya tambayi wadanda a ke zargin kuma sun amsa duk laifukan da a ke tuhumarsu da aikatawa.
Sai dai mai shari’a Sarki Yola, ya bayar da umarni a koma wajen ‘yan sanda, domin yin bincike a kai. Wanda za a dawo ranar 13 ga watan Janairu na 2021.