fidelitybank

A na fakon ƴan majalisar ƙasar nan su kai musu hari, in ji SSS

Date:

 

 

 

Hukumar Ƴan sandan Farin Kaya, SSS ta shawarci ƴan majalisar taraiya da na jihohi, sanannun mutane, matafiya da ɗalibai da su ka zo hutu da su kiyaye su ka guji guraren da ɓatagari za su iya illata su.

Dakta Peter Afunanya, kakakin hukumar SSS ne ya bada wannan shawarar a taron manema labarai a yau Talata a Abuja.

Ya kuma gargaɗi masu ɗaukar nauyin garkuwa da mutane, fashin daji, ta’addanci, da sauran laifuka da su gaggauta daina wa.

“Bari na sake nanata wa cewa duk waɗanda su ke ɗaukar nauyin garkuwa da mutane fashin daji, ta’addanci, da sauran laifuka da su gaggauta canja tunani.

“Su masu aikata waɗan nan laifukan, ko a Arewa ko a Kudu, sun san kansu. Babu tantama cewa tura ta kai bango, sabo da haka yanzu lokaci ya yi da za a sanya ƙafar wando ɗaya da su,”

Afunanya ya yi kira ga iyaye da su sanya idanu a kan ƴaƴan su yayin da su ke dawowa hutun Kirsimeti.

Ya kuma yi kira ga malamai da sarakunan gargajiya da su kame harsunan su daga munanan maganganu, in da ya ja kunnen su game da yin kalaman tunzuri.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp