fidelitybank

A na fakewa da biyan kuɗin fansa a ɗebe dukiyar gwamnati — Kwamishina

Date:

 

Kwamishinan Shari’a na Jihar Kwara, Salman Jawando ya yi zargin cewa “a na ɗebe kuɗaɗen gwamnati bayan fakewa da cewa dole a bayar da kuɗin fansa ga masu garkuwa da mutane sannan su saki waɗanda su ka kama.”
Jawando ya yi wannan zargi ne a ranar Litinin a yayin taron ranar Shari’a na 2021/2022 da kuma bikin sallamar alaƙalan da su ka yi murabus da ga aiki a Ilori.
Jawando ya bi sahun waɗanda su ke kira da a yi wa ɗaukacin fannin Shari’a garambawul a Nijeriya.
“Rashin tsaro a ƙasar nan ya yi ƙamari har ta kai ga ba wan da ya ke yin Bacci da ido biyu a rufe,” in ji shi.
“Batun kuɗin fansa ga masu garkuwa da mutane ya zamo wata hanya 5a samun maƙudan kuɗaɗe da ɓatagari su ke yi da haɗin kan wasu mugayen mutane.
“Ya zamo wata hanya da a ke kwashe kuɗaɗen gwamnati inda a ke fakewa da biyan kuɗin fansa da ƙaryar cewa wai idan ba a biya ba to waɗanda a ka sace ɗin za su shiga uku.
“Ɓangaren Shari’a wanda ya zamana nan ne madogarar talaka a ƙasar nan ya kamata ya tashi ya yi tashi tsaye domin tserar da ƴan ƙasa da ga wannan bala’in da ke cinye tsokokin jikkunan mu,” in ji Jawando.
Kwamishinan ya nuna mamaki da yadda a ke jan ƙafa a shari’ar masu garkuwa da mutane, inda ya baiyana cewa hakan na nuni da cewa dole a yi garambawul a gaba ɗaya ɓangaren Shari’a a ƙasar nan.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp