fidelitybank

A na fakewa da biyan kuɗin fansa a ɗebe dukiyar gwamnati — Kwamishina

Date:

 

Kwamishinan Shari’a na Jihar Kwara, Salman Jawando ya yi zargin cewa “a na ɗebe kuɗaɗen gwamnati bayan fakewa da cewa dole a bayar da kuɗin fansa ga masu garkuwa da mutane sannan su saki waɗanda su ka kama.”
Jawando ya yi wannan zargi ne a ranar Litinin a yayin taron ranar Shari’a na 2021/2022 da kuma bikin sallamar alaƙalan da su ka yi murabus da ga aiki a Ilori.
Jawando ya bi sahun waɗanda su ke kira da a yi wa ɗaukacin fannin Shari’a garambawul a Nijeriya.
“Rashin tsaro a ƙasar nan ya yi ƙamari har ta kai ga ba wan da ya ke yin Bacci da ido biyu a rufe,” in ji shi.
“Batun kuɗin fansa ga masu garkuwa da mutane ya zamo wata hanya 5a samun maƙudan kuɗaɗe da ɓatagari su ke yi da haɗin kan wasu mugayen mutane.
“Ya zamo wata hanya da a ke kwashe kuɗaɗen gwamnati inda a ke fakewa da biyan kuɗin fansa da ƙaryar cewa wai idan ba a biya ba to waɗanda a ka sace ɗin za su shiga uku.
“Ɓangaren Shari’a wanda ya zamana nan ne madogarar talaka a ƙasar nan ya kamata ya tashi ya yi tashi tsaye domin tserar da ƴan ƙasa da ga wannan bala’in da ke cinye tsokokin jikkunan mu,” in ji Jawando.
Kwamishinan ya nuna mamaki da yadda a ke jan ƙafa a shari’ar masu garkuwa da mutane, inda ya baiyana cewa hakan na nuni da cewa dole a yi garambawul a gaba ɗaya ɓangaren Shari’a a ƙasar nan.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...
X whatsapp