Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya bayar da umarnin a kama wani mawaki mai suna, Mohammad Danshanawa da ya yabi wani shugaban ‘yan ta’adda, Bello Turji a wakarsa, kamar.
SaharaReporters ta rawaito cewa, a cikin wani faifan sauti na waka, Danshawa ya yabawa dan ta’addan, Turji, ya na mai bayyana shi a matsayin “Zaki, wanda ba a taba taba shi ba, kuma babban shugaba”.
Umarnin na gwamnan ya zo ne kwanaki Uku bayan wakar ta fara yaduwa a shafukan sada zumunta da dama.
A cewar saharareporters, da ya ke tsokaci kan wakar, gwamna Tambuwal, ya ce, “Mun ba da umarnin a kama shi ne, domin a kawo masa cikas, dalilin da ya sa na ba da shawarar cewa shugaban kasa da babban kwamandan rundunar soji su yi la’akari da su, domin a wuraren da a ke fama da kalubalen tsaro, mazauna yankin su na son a horar da su kan sarrafa makamai”.
Wasu mazauna Sokoto da suka yi tir da wakar, sun bayyana abin da mawakin ya yi a matsayin rashin kishin kasa