fidelitybank

A gaggauta gudanar da binciken turmutsutsun da aka yi a wasan Kamaru – Paul Biya

Date:

Shugaban kasar Kamaru Paul Biya, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan abin da ya janyo aka yi turmutsutsun da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum takwas a wajen filin wasa a babban birnin kasar Yaoundé kafin wani wasana gasar cin kofin Afirka.

Wata sanarwa da gwamnati ta fitar ta ce, binciken zai sa a gano abin da ya haddasa lamarin.

Turmutsutsun ya faru ne a lokacin da magoya baya suka yi kokarin kutsawa cikin filin wasan Olembe kafin karawar Kamaru da Komoros (Comoros) .

Bayan wadanda suka rasa ransu, wasu mutum talatin kuma sun ji rauni.

Ba a dai tsara cewa, mutane da yawa za su shiga kallon wasan ba, saboda matakan kariya na cutar korona, amma wadanda suka ga abin da ya faru sun ce tarin magoya baya sun je domin shiga cikin filin.

Hukumar kwallon kafa ta Afirka (Caf), wadda ta shirya gasar ita ma ta kaddamar da nata binciken.

Kamaru wadda ta yi nasarar zuwa wasan dab da na kusa da karshe bayan ta doke Komoros da ci 2-1, a wasan, yanzu za ta kara da Gambia, wadda ita kuma ta ci Guinea 1-0.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naÉ—in...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa Æ´an wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...
X whatsapp