Shugaban kasar Kamaru Paul Biya, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan abin da ya janyo aka yi turmutsutsun da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum takwas a wajen filin wasa a babban birnin kasar Yaoundé kafin wani wasana gasar cin kofin Afirka.
Wata sanarwa da gwamnati ta fitar ta ce, binciken zai sa a gano abin da ya haddasa lamarin.
Turmutsutsun ya faru ne a lokacin da magoya baya suka yi kokarin kutsawa cikin filin wasan Olembe kafin karawar Kamaru da Komoros (Comoros) .
Bayan wadanda suka rasa ransu, wasu mutum talatin kuma sun ji rauni.
Ba a dai tsara cewa, mutane da yawa za su shiga kallon wasan ba, saboda matakan kariya na cutar korona, amma wadanda suka ga abin da ya faru sun ce tarin magoya baya sun je domin shiga cikin filin.
Hukumar kwallon kafa ta Afirka (Caf), wadda ta shirya gasar ita ma ta kaddamar da nata binciken.
Kamaru wadda ta yi nasarar zuwa wasan dab da na kusa da karshe bayan ta doke Komoros da ci 2-1, a wasan, yanzu za ta kara da Gambia, wadda ita kuma ta ci Guinea 1-0.