fidelitybank

A gaggauta gudanar da binciken turmutsutsun da aka yi a wasan Kamaru – Paul Biya

Date:

Shugaban kasar Kamaru Paul Biya, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan abin da ya janyo aka yi turmutsutsun da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum takwas a wajen filin wasa a babban birnin kasar Yaoundé kafin wani wasana gasar cin kofin Afirka.

Wata sanarwa da gwamnati ta fitar ta ce, binciken zai sa a gano abin da ya haddasa lamarin.

Turmutsutsun ya faru ne a lokacin da magoya baya suka yi kokarin kutsawa cikin filin wasan Olembe kafin karawar Kamaru da Komoros (Comoros) .

Bayan wadanda suka rasa ransu, wasu mutum talatin kuma sun ji rauni.

Ba a dai tsara cewa, mutane da yawa za su shiga kallon wasan ba, saboda matakan kariya na cutar korona, amma wadanda suka ga abin da ya faru sun ce tarin magoya baya sun je domin shiga cikin filin.

Hukumar kwallon kafa ta Afirka (Caf), wadda ta shirya gasar ita ma ta kaddamar da nata binciken.

Kamaru wadda ta yi nasarar zuwa wasan dab da na kusa da karshe bayan ta doke Komoros da ci 2-1, a wasan, yanzu za ta kara da Gambia, wadda ita kuma ta ci Guinea 1-0.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naÉ—a shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp