fidelitybank

A dakata da baiwa gwamnatin Kano bashi – Abba

Date:

Zaɓaɓɓen gwamnan Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya shawarci masu bai wa gwamnatin jihar bashi a wannan lokaci da su dakata.

A wata sanarwa da sakataren yaɗa labaransa, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, gwamnan mai jiran gado ya shawarci masu ba da bashi na cikin gida da na ƙetare ga gwamnatin Kano mai barin gado, su dakatar da hakan daga 18 ga watan Maris zuwa 29 ga watan Mayu.

Sanarwar ta ci gaba da cewa sabuwar gwamnatin ba za ta yi la’akari da bashin da jihar ta karɓa ba, matuƙar ba a sanar da ita game da hakan ba.

Ta kuma ce masu bin gwamnatin jihar bashi, su kwan da sanin cewa za a sake nazarin ƙa’idojin bashin da suka bai wa gwamnati mai barin gado, bayan kammala bincike a kan duk bashin da ake bin Kano.

A tsakiyar wannan mako ma, zaɓaɓɓen gwamnan ya fitar da irin wannan sanarwa da ya ce shawara ce ga masu gine-gine a filayen gwamantin jihar, inda ya nemi su dakata.

Karanta Wannan: Masu yanke-yanken fili da gini ko ina a Kano ku tsaya cak – Sabon Gwamna

Har yanzu mulki na ne ba na Abba ba – Ganduje

Sai dai, washe gari da fitar da shawarar, gwamnan Kano mai barin gado, Abdullahi Umar Ganduje ya mayar da martani, yana cewa ya kamata gwamnan mai jiran gado ya yi haƙuri, ya daina fitar da sanarwar hukuma da sunan shawara.

A sanarwar da ya fitar, kwamishinan yaɗa labaran jihar, Muhammad Garba ya ce abin da zaɓaɓɓen gwamnan ya yi, tamkar ba da umarni ne a kan wani batu da ya shafi manufar gwamnati, a daidai lokacin da gwamna mai ci har yanzu ke da cikakken iko.

Lamarin da ka iya zama riga mallam masallaci

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp