fidelitybank

A ci gaba da tsare matar Abdulmalik a gidan gyaran hali – Kotu

Date:

Kotu ta umarci ‘yan sanda su ci gaba da tsare Jamila Muhammad, matar mutumin da ake zargi da kisan Hanifa Abubakar mai shekara 5 a Jihar Kano.

A na zargin Jamila mai shekara 30 da haɗa baki wajen ɓoye yarinyar da mijinta Abdulmalik Tanko ya sato, da ƙulla makirci, da sace mutum, da kuma kisan kai.

Da yake karanto tuhumar da ake yi mata, lauya mai shigar da ƙara ya ce ana zargin ta da ɓoye wadda aka yi garkuwa da ita tsawon kwana biyar.

Jamila ta ƙaryata rahoton farko da aka bayar wanda ya zarge ta da ɓoye Hanifa a gidanta.

Idan ba a manta ba, Abdulmalik ya faɗa wa ‘yan sanda cewa bayan ya sace Hanifa ya kai ta wajen matarsa ne, inda ta zauna a gidan kafin daga baya ya kashe kuma ya binne ta a farfajiyar makarantarsa da ke Kwanar Dakata ta Ƙaramar Hukumar Nasarawa a birnin Kano.

Kotun Majistaren da ke Gidan Murtala ta ɗage zaman zuwa 2 ga watan Fabarairu tare da uamrtar ‘yan sanda su ci gaba da tsare Jamila.

Gwamnan Kano Abdullahi Ganduje ya ce, a shirye yake ya sanya hannu kan zartar da hukunci idan kotu ta yanke wa Abdulmalik hukuncin kisa.

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp