Kotu ta umarci ‘yan sanda su ci gaba da tsare Jamila Muhammad, matar mutumin da ake zargi da kisan Hanifa Abubakar mai shekara 5 a Jihar Kano.
A na zargin Jamila mai shekara 30 da haɗa baki wajen ɓoye yarinyar da mijinta Abdulmalik Tanko ya sato, da ƙulla makirci, da sace mutum, da kuma kisan kai.
Da yake karanto tuhumar da ake yi mata, lauya mai shigar da ƙara ya ce ana zargin ta da ɓoye wadda aka yi garkuwa da ita tsawon kwana biyar.
Jamila ta ƙaryata rahoton farko da aka bayar wanda ya zarge ta da ɓoye Hanifa a gidanta.
Idan ba a manta ba, Abdulmalik ya faɗa wa ‘yan sanda cewa bayan ya sace Hanifa ya kai ta wajen matarsa ne, inda ta zauna a gidan kafin daga baya ya kashe kuma ya binne ta a farfajiyar makarantarsa da ke Kwanar Dakata ta Ƙaramar Hukumar Nasarawa a birnin Kano.
Kotun Majistaren da ke Gidan Murtala ta ɗage zaman zuwa 2 ga watan Fabarairu tare da uamrtar ‘yan sanda su ci gaba da tsare Jamila.
Gwamnan Kano Abdullahi Ganduje ya ce, a shirye yake ya sanya hannu kan zartar da hukunci idan kotu ta yanke wa Abdulmalik hukuncin kisa.