fidelitybank

Gamayyar kungiyoyin ma’aikatan sufuri sun fasa shiga yajin aiki

Date:

Gamayyar kungiyoyin ma’aikatan da ke aiki a bangaren sufurin jirgin sama a Najeriya sun janye yajin aikin da suka shirya yi.

Kungiyoyin sun fasa daukar matakin ne bayan da suka rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeniya da gwamnatin Najeriya yayin wani zama na musamman da aka yi a shalkwatar ma’aikatar kwadago ta Najeriya a ranar Litinin a Abuja.

A cewar BBC, manyan batutuwan da suka janyo barazanar yajin aikin sun hada da rashin biyan ma’aikata sabon albashi mafi kankanta, wanda tun 2019 ya kamata a fara biya.

Batu na biyu kuma shi ne jinkirin fara amfani da sharuddan aiki kamar yadda suka shafi ma’aikatan da ke aiki a hukumomin gwamnatin tarayyar Najeriya.

Ministan kwadago da ayyukan yi, Chris Ngige ya tabbatar da kulla yarjejeniyar:

“Mun yarda tsakaninmu cewa hukumar da ke tsara albashin ma’aikata a Najeriya za ta aika wa dukkan ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya – har da wadanda ba ma’aikatan gwamnati ne ba – wata wasika da ke fayyace matakan da ya dace su dauka kan biyan albashin ma’aikata karkashin dokar Albashi ta bai daya na 2019.”

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp