fidelitybank

Kotu ta daure magidancin da ya yi wa ‘yar sa ciki

Date:

Kotu a jihar Legas ta daure wani mahaifi mai shekaru 42, zai sha ɗaurin rai-da-rai ba tare da zaɓin biyan tara ba, bayan kotun hukunta laifukan cin zarafi ta same shi da laifin yi wa ‘yarsa mai shekara 15 fyaɗe da kuma yi mata ciki.

Kotun da ke Jihar Legas ta kama Ekpo Lawrence da laifin ne a jiya Alhamis, bayan da mai shari’a, Abiola Soladoye ta ce, kotun ta yi nasarar tabbatar da zargin da gwamnatin Legas ta gabatar kan mista Lawrence.

Kamfanin dillancin labarai na NAN ya rawaito cewa, mai shari’ar ta ce, hujjojin da masu shigar da ƙarar suka bayar sun yi daidai, yayin da shi kuma wanda ake zargi ya yi ta sauya zance.

Ta ƙara da cewa, musanta zargin da mutumin ya yi da gangan ne, domin ya karkatar da hankalin kotu. Ta ce, “Abain kunyar da wanda ake zargin ya aikata ya ƙazanta, kuma ba abin yafewa ba ne a ƙarƙashin sashe na 137 na Dokokin Manyan Laifuka na Jihar Legas na shekarar 2015, sannan abin Allah-wadai ne ta kowace fuska,” in ji Mai Shari’a Soladoye.

kamfanin dillancin labarai na Kasa NAN ta rawaito cewa, masu shigar da ƙara sun ce mutumin ya aikata laifin ne tsakanin watan Disambar shekarar 2018 zuwa watan Yunin 2019.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp