fidelitybank

Kotu ta daure magidancin da ya yi wa ‘yar sa ciki

Date:

Kotu a jihar Legas ta daure wani mahaifi mai shekaru 42, zai sha ɗaurin rai-da-rai ba tare da zaɓin biyan tara ba, bayan kotun hukunta laifukan cin zarafi ta same shi da laifin yi wa ‘yarsa mai shekara 15 fyaɗe da kuma yi mata ciki.

Kotun da ke Jihar Legas ta kama Ekpo Lawrence da laifin ne a jiya Alhamis, bayan da mai shari’a, Abiola Soladoye ta ce, kotun ta yi nasarar tabbatar da zargin da gwamnatin Legas ta gabatar kan mista Lawrence.

Kamfanin dillancin labarai na NAN ya rawaito cewa, mai shari’ar ta ce, hujjojin da masu shigar da ƙarar suka bayar sun yi daidai, yayin da shi kuma wanda ake zargi ya yi ta sauya zance.

Ta ƙara da cewa, musanta zargin da mutumin ya yi da gangan ne, domin ya karkatar da hankalin kotu. Ta ce, “Abain kunyar da wanda ake zargin ya aikata ya ƙazanta, kuma ba abin yafewa ba ne a ƙarƙashin sashe na 137 na Dokokin Manyan Laifuka na Jihar Legas na shekarar 2015, sannan abin Allah-wadai ne ta kowace fuska,” in ji Mai Shari’a Soladoye.

kamfanin dillancin labarai na Kasa NAN ta rawaito cewa, masu shigar da ƙara sun ce mutumin ya aikata laifin ne tsakanin watan Disambar shekarar 2018 zuwa watan Yunin 2019.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp