Ma’aikatan ‘yan jarida ne suka cika titunan kasar Mexico domin gudanar da zanga-zanga kan kashe takwarorinsu a kasar.
‘Yan jaridar sun yi kiran a kawo karshen bai wa jami’an gwamnati kariya.
Wakilin BBC ya shaida cewa, an yi zanga-zangar a biranen kasar ciki har da Tekuana da Kankun da kuma Gwalarahara.
‘Yan jaridar gidajen radiyon yankin sun fito, domin nuna fushi kan kisan Loures Maldonado daidai lokacin da ta isa gida daga wurin aiki.
A na ta sukar matakin shugaba Andres Manuel Lopez Obrador na yin gum da bakinsa da gaza bai wa ‘yan jaridar Mexico kariya.