Hukumar Hisbah ta jihar Jigawa ta kwace kwalaben giya 1,906 a wani sumamen da ta kai a lokuta daban-daban a fadin jihar a shekarar da ta gabata, 2021.
Kwamandan rundunar, Mallam Ibrahim Dahiru ne ya shaidawa kamfanin dillancin labaran kasa NAN, a Dutse, babban birnin jihar, a ranar Talata, 25 ga watan Janairun 2022.
Mallam Ibrahim ya ce, sun yi nasarar kwace giyar ne a otal-otal da wuraren shan barasa daban-daban a fadin jihar.
Shugaban Hisbar ya kuma ce, “Mun kama mutum 92 da muke zargi da aikata laifuka na badala daban-daban, wadanda suka hada da karuwai a lokacin sumame. Laifukan da ake zargin mutanen sun aikata sun hada da caca da yawan-ta-zubar da shirya liyafar casu a lokacin biki da sauransu”, in ji kwamandan.
Haka kuma ya ce a tsawon lokacin Hisbah ta rufe gidajen karuwai.
Mallam Ibrahim ya kara da cewa, an mika kwalaben giyar da aka kwace da mutanen da aka kama ga ‘yan sanda, domin kara bincike.