fidelitybank

Hisba ta kama kwalaben giya 1,906 a Jigawa

Date:

Hukumar Hisbah ta jihar Jigawa ta kwace kwalaben giya 1,906 a wani sumamen da ta kai a lokuta daban-daban a fadin jihar a shekarar da ta gabata, 2021.

Kwamandan rundunar, Mallam Ibrahim Dahiru ne ya shaidawa kamfanin dillancin labaran kasa NAN, a Dutse, babban birnin jihar, a ranar Talata, 25 ga watan Janairun 2022.

Mallam Ibrahim ya ce, sun yi nasarar kwace giyar ne a otal-otal da wuraren shan barasa daban-daban a fadin jihar.

Shugaban Hisbar ya kuma ce, “Mun kama mutum 92 da muke zargi da aikata laifuka na badala daban-daban, wadanda suka hada da karuwai a lokacin sumame. Laifukan da ake zargin mutanen sun aikata sun hada da caca da yawan-ta-zubar da shirya liyafar casu a lokacin biki da sauransu”, in ji kwamandan.

Haka kuma ya ce a tsawon lokacin Hisbah ta rufe gidajen karuwai.

Mallam Ibrahim ya kara da cewa, an mika kwalaben giyar da aka kwace da mutanen da aka kama ga ‘yan sanda, domin kara bincike.

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na É—aukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Æ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Æ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Æ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faÉ—a ADC

Tsohon É—an jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

ÆŠan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp