fidelitybank

Mutane 8 sun mutu yayin shiga filin wasa a Kamaru

Date:

Rahotanni na nuni da cewa, akalla mutune takwas ake zargin sun mutu yayin da 38 suka jikkata, sakamakon wani turmutsitsi da ya auku a wajen filin da ake buga gasar cin kofin nahiyar Afirka ta Afcon a Kamaru.

Hotunan bidiyo sun nuna yadda ‘yan kallo suka rinÆ™a kokowar shiga fili wasa na Paul Biya da ke birnin Yaounde.

Naseri Paul Biya, wanda shi ne gwamnan yankin tsakiyar Kamaru, ya ce akwai yiwuwar a samu karin mutanen da abin ya shafa, a cewar kamfanin labarai na AP.

Wani rahoton kuma na cewa akwai yara da dama da suka suma.

Filin wasan na iya daukar mutum dubu 60, amma saboda matakan da ake É—auka saboda annobar korona ba a yarda a haura kashi 80 cikin 100 na wannan adadin ba.

Jami’ai sun ce mutum dubu 50 ne suka yi kokarin shiga filin wasan domin kallo.

Malaman jinya Olinga Prudence ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na AP cewa, wasu daga cikin mutanen da suka jikkata na cikin yanayi na galabaita.

Hukumar kwallon kasashen Afirka, CAF a wata sanarwa ta ce tana bincike kan lamarin domin samun ƙarin bayanai kan ainihin abin da ya faru.

An dai fafata a zagaye na biyu na gasar tsakanin Cameroon da Comoros duk da faruwar wannan al’amari, kuma mai karban bakwancin wasan ta yi nasara da 2-1.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na É—aukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Æ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Æ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Æ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faÉ—a ADC

Tsohon É—an jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

ÆŠan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp