Ma’aikatar wasanni ta kasar Ghana, ta umurci hukumar kwallon kafar Ghana da ta kori mai horar da ‘yan wasanta dan kasar Serbia, Milovan Rajevac.
Jaridar African Sports Today ta rawaito cewa, matakin na hukumar wanda ta yi taron gaggawa a ranar Juma’a, bayan biyo bayan kasa tabuka abin arziki da Ghana ta yi a gasar cin kofin nahiyar Afirka da ake gudanarwa a kasar Kamaru,
Duk da rashin son korar Rajevac da hukumar ta FA ta yi, da alama ma’aikatar ta yi nasara a ganawar da ake yi kan makomar dan wasan na Serbia.
Rajevac a karon farko da Black Stars ya jagoranci Ghana zuwa wasan karshe na AFCON 2010 da kuma Quarter final na gasar cin kofin duniya ta 2010.
Wasansa na biyu bai tafi yadda ake tsammani ba, yayin da Ghana ta fice daga gasar AFCON ta 2021 ba tare da samun nasara ba, irinsa na farko a tarihin Black Stars.
Hukumar kwallon kafar Ghana za ta fitar da sanarwa game da ci gaban nan ba da jimawa ba.