Gwamnatin Jihar Legas ta sanya hannu a kan wata sabuwar doka da za ta tattare harajin da take karba wuri guda daga masu motocin haya a tashoshin mota da garejin Jihar.
An dai cimma yarjejeniyar dokar ne tsakanin gwamnatin Jihar da na kananan hukumomi da kungiyoyin sufuri daban-daban da kuma wasu hukumomin gwamnatin Jihar.
A cewar kwamishinan kudi na Jihar, Dr. Rabi’u Olowo, ya ce harajin, wanda aka yanke shi a N800, ya kunshi dukkan kudaden da hukumomin Jihar suke karba daga direbobin a matsayin kudin shiga.
Ya ce, sabuwar dokar za ta fara aiki ne nan take.
Hakan dai na nufin kowacce motar haya za ta rinka biyan N800 a kullum, wato N24,000 a kowane wata, jimlar N292,000 ke nan a shekara. A cewar Aminiya.