fidelitybank

Mu tashi tsaye wajen tunkarar tsaro a Najeriya -Ganduje

Date:

Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya yi kira ga rundunar sojojin Najeriya da su tashi tsaye wajen tunkarar kalubalen rashin tsaro da ke addabar kasar, tare da kawar da masu aikata laifuka a kasar.

Gwamnan ya yabawa jami’an tsaro a kasar nan kan ayyukan sadaukar da kai da suke yi wajen wanzar da zaman lafiya a kasar, inda ya bukace su da su yi aiki tukuru da tabbatar da dunkulewar Nijeriya tare da tabbatar da tsaro.

Da ya ke jawabi a ranar Asabar a Kano, bayan ya ajiye fure a wajen taron tunawa da ranarĀ  sojojin kasar, Ganduje ya bayyana cewa, dangane da yadda ake baiwa jaruman da suka shude, jami’an tsaro a Najeriya za su dauki nauyin da ya rataya a wuyansu.

ā€œBabu shakka wannan rana ce da ya kamata mu rinka tunawa a kowace shekara. Ina taya masu shirya taron murna da suka shirya taron tsawon kwanaki bakwai da suka gabata kuma yau an kammala komai.

ā€œMuhimmancin wannan rana shi ne tunawa da wadanda suka yi yakin basasar Najeriya, domin ganin Najeriya ta kasance kasa daya. Babu shakka muna amfana daga abin da suka yi a baya domin haka ya na da kyau mu tuna da su.

ā€œHaka zalika idan aka yi la’akari da kalubalen tsaro da muke fama da shi a kasar nan, wannan rana na da matukar muhimmanci ta yadda jami’an tsaronmu za su dauki nauyin da ya rataya a wuyansu da gaske, ta yadda za mu ci gaba da wanzuwa a matsayin kasa daya na kawar da kanmu daga masu aikata laifuka a cikinmu,ā€ in ji Ganduje. .

Sauran wadanda suka halarci bikin tunawa da ranar sun hada da mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero da manyan hafsoshin Soja da Sojojin Sama, na ruwa da NSCDC, da Kwamishinan ā€˜yan sanda.

Sauran su ne matan sojoji, kungiyoyin ma’aikatan soja da suka yi ritaya da iyalansu.

 

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

ʘungiyar kare haʙʙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buʙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ʙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko Ę“anʙwallon...

Sunderland ta ɗauko Ę“anʙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ʙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp