fidelitybank

Mu tashi tsaye wajen tunkarar tsaro a Najeriya -Ganduje

Date:

Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya yi kira ga rundunar sojojin Najeriya da su tashi tsaye wajen tunkarar kalubalen rashin tsaro da ke addabar kasar, tare da kawar da masu aikata laifuka a kasar.

Gwamnan ya yabawa jami’an tsaro a kasar nan kan ayyukan sadaukar da kai da suke yi wajen wanzar da zaman lafiya a kasar, inda ya bukace su da su yi aiki tukuru da tabbatar da dunkulewar Nijeriya tare da tabbatar da tsaro.

Da ya ke jawabi a ranar Asabar a Kano, bayan ya ajiye fure a wajen taron tunawa da ranarĀ  sojojin kasar, Ganduje ya bayyana cewa, dangane da yadda ake baiwa jaruman da suka shude, jami’an tsaro a Najeriya za su dauki nauyin da ya rataya a wuyansu.

ā€œBabu shakka wannan rana ce da ya kamata mu rinka tunawa a kowace shekara. Ina taya masu shirya taron murna da suka shirya taron tsawon kwanaki bakwai da suka gabata kuma yau an kammala komai.

ā€œMuhimmancin wannan rana shi ne tunawa da wadanda suka yi yakin basasar Najeriya, domin ganin Najeriya ta kasance kasa daya. Babu shakka muna amfana daga abin da suka yi a baya domin haka ya na da kyau mu tuna da su.

ā€œHaka zalika idan aka yi la’akari da kalubalen tsaro da muke fama da shi a kasar nan, wannan rana na da matukar muhimmanci ta yadda jami’an tsaronmu za su dauki nauyin da ya rataya a wuyansu da gaske, ta yadda za mu ci gaba da wanzuwa a matsayin kasa daya na kawar da kanmu daga masu aikata laifuka a cikinmu,ā€ in ji Ganduje. .

Sauran wadanda suka halarci bikin tunawa da ranar sun hada da mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero da manyan hafsoshin Soja da Sojojin Sama, na ruwa da NSCDC, da Kwamishinan ā€˜yan sanda.

Sauran su ne matan sojoji, kungiyoyin ma’aikatan soja da suka yi ritaya da iyalansu.

 

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ę“ansandan jihar Kaduna, sun buʙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ʙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ā€˜Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ʙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ā€˜yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp