Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya yi kira ga rundunar sojojin Najeriya da su tashi tsaye wajen tunkarar kalubalen rashin tsaro da ke addabar kasar, tare da kawar da masu aikata laifuka a kasar.
Gwamnan ya yabawa jamiāan tsaro a kasar nan kan ayyukan sadaukar da kai da suke yi wajen wanzar da zaman lafiya a kasar, inda ya bukace su da su yi aiki tukuru da tabbatar da dunkulewar Nijeriya tare da tabbatar da tsaro.
Da ya ke jawabi a ranar Asabar a Kano, bayan ya ajiye fure a wajen taron tunawa da ranarĀ sojojin kasar, Ganduje ya bayyana cewa, dangane da yadda ake baiwa jaruman da suka shude, jamiāan tsaro a Najeriya za su dauki nauyin da ya rataya a wuyansu.
āBabu shakka wannan rana ce da ya kamata mu rinka tunawa a kowace shekara. Ina taya masu shirya taron murna da suka shirya taron tsawon kwanaki bakwai da suka gabata kuma yau an kammala komai.
āMuhimmancin wannan rana shi ne tunawa da wadanda suka yi yakin basasar Najeriya, domin ganin Najeriya ta kasance kasa daya. Babu shakka muna amfana daga abin da suka yi a baya domin haka ya na da kyau mu tuna da su.
āHaka zalika idan aka yi laāakari da kalubalen tsaro da muke fama da shi a kasar nan, wannan rana na da matukar muhimmanci ta yadda jamiāan tsaronmu za su dauki nauyin da ya rataya a wuyansu da gaske, ta yadda za mu ci gaba da wanzuwa a matsayin kasa daya na kawar da kanmu daga masu aikata laifuka a cikinmu,ā in ji Ganduje. .
Sauran wadanda suka halarci bikin tunawa da ranar sun hada da mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero da manyan hafsoshin Soja da Sojojin Sama, na ruwa da NSCDC, da Kwamishinan āyan sanda.
Sauran su ne matan sojoji, kungiyoyin maāaikatan soja da suka yi ritaya da iyalansu.