Aƙalla mutum biyar aka kashe yayin wani sabon rikicin makiyaya da manoma a yankin Imeko-Afon a jihar Ogun.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, rikicin ya faru ne bayan wasu ƴan watanni da faruwar makamcinsa a Yewa da ke jihar. An kuma banka wa gidaje da gonaki da dama wuta a yayin
rikiciRahotanni sun ce, rikicin ya faro ne a ranar Laraba, lokacin da mutanen wani gari da ake kira Aworo a ƙaramar hukumar Yewa suka fatattaki makiyaya zuwa wani ƙauye da ake kira Idifo, tare da kashe uku daga cikinsu.
Suna zargin makiyayan ne da lalata gonakinsu da wuraren shan ruwa sakamakon ƙyale shanunsu suna kiwo.
Kakakin ‘yan sanda na jihar Abimbola Oyeyemi, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Asabar, amma ya ce babu wanda aka kama ya zuwa yanzu.